- Za a karrama mashahuriyar mawakiya Fati Nijar a wani babban taro na mata da za a yi a Kano
- Mawakiyar ‘yar asalin Jamhuriyar Nijar ta shahara ne a wakokin zamani musamman a taron shagulgulan biki
- Kwanan baya ne masarautar Borgu ta karrama mawakiyar da sarautar gargajiya inda ‘yan uwa da abokan arzikin da kuma abokan sana’a suka halarta

Likkafar Binta Labaran wacce aka fi sani da Fati Nijar ta yi gaba da wata karramawa da za a yiwa matashiyar mawakiyar a ranar Alhamis a 13 ga watan Oktoba na shekarar 2016 a garin Kano.
Kungiyar tallafawa mata a harkar kasuwanci da sana’a BWAEF ce ta shirya karrama Fati tare da wasu matan da suka yi fice a harkar kasuwanci da sana’a, suka kuma yi abin kuzo-ku-gani.
A cewar wani na hannun daman mawakiyar, Binta Labaran ‘yar asalin jamhuriyar Nijar ce, ta yi fice a wakokin zamani a inda wakokinta suka yi farin jini da tsakanin matasa, Fati ta kuma yi suna wakokin da ta yi wa amare da ango a bukuwa a inda ta ke zuwa ta rera kai tsaye.

Rahotanni na cewa, Fati ‘yar asalin jamhuriyar Nijar ta zo Kano ne a shekarun 1990 da ziyara, da kuma aniyar fitowa a fina-finan Hausa, ta samu kanta a waka ne a sakamakon hulda da Abubakar Sani mawakin finafinan da kuma sauransu da suke tashe a lokacin.
A kwanan baya ne masarautar Borgu a jihar Naija ta karrama Fati da sarautar gargajiya domin yabawa da irin gudunmawar da ta ke bayarwa wajen bunkasa harshen Hausa a wake-wakenta. An kuma gudanar da kasaitaccen bikin nadin sarautar a garin, inda ‘yan uwa da abokan arziki da kuma abokan sana’arta suka halarta.
Asali: Legit.ng
ncG1vNJzZmigkarAonrLnp6irF6jtHCFmG1vcG9dma6vsMCloKdlm5a7r8XWqKadZaqWerq1jJugpKGeYrOiwMhmpaKikad6rK3NqGWhrJ2h